Sarkin Ingila, Sarki Charles III, ya jinjina wa Najeriya, inda ya ce alaƙa tsakanin ƙasashen biyu na ƙara haɓaka ta ɓangaren tattalin arziki da fahimtar juna, sannan ya bayyana ƙasar a matsayin ƙasa mai ƙarfin tattalin arziki.
Sarki Charles ya bayyana haka ne a lokacin da yake gabatar da jawabin maraba ga shugaban Najeriya Bola Tinubu da matarsa Oluremi Tinubu da sauran tawagarsa a Fadar Windsor Castle.
Ya ce masarautarsa na godiya ga Tinubu da ya kai ziyarar a lokacin azumi, sannan ya yi waiwayen lokacin da ya ziyarci Najeriya a 2018.
"A lokacin na gana da wasu sarakunan ƙasarka masu daraja irin su Sultan na Sokoto da Ooni na Ife da Sarkin Kano da sarakunan Warri da Onitsha. Na gane wa idona cewa ƙasar na samun gagarumin cigaba."
A Birtaniya akwai mutane da dama ƴan asalin Najeriya, waɗanda suke zaune suna gudanar da harkokinsu na kasuwanci da wasu a ɓangaren kimiyya da shari'a da ƙirƙira da fasaha da aikin gwamnati, kuma suna samun nasara sosai.
"Wannan ziyarar na ƙara nuna cewa Najeriya na ƙoƙarin sa hannu a cigaban Birtaniya, kamar yadda Birtaniya ke sa hannu domin cigaban Najeriya. Ƴan Najeriya sun kashe fam miliyan 178 a Birtaniya a 2024, sannan aƙalla mutum 251,000 ne suka je Najeriya daga Birtaniya, inda suma suka kashe kuɗaɗe masu yawa."
"Alaƙar da ke tsakanin ƙasashenmu ta wanke ni ne in wanke ka, wadda dukkanmu muke samun riba, sannan kuma alaƙa ce daɗaɗɗiya."
"Da yammacin na, mai girma shugaban ƙasa ni da kai mun gane wa idon abin koyi mai kyau a ganawarmu da jagororin addinai na Musulunci da Kiristanci na Birtaniya. Taron ya yi ma'ana sosai, musamman kan abin da Najeriya ta daɗe tana nunawa cewa mutane mabambanta addini za su iya rayuwa tare cikin zaman lafiya da lumana."
Sarki Charles ya ƙara da cewa, "Kasarka na da ƙarfin tattalin arziki, tana da dimɓin tarihin al'adu da murya mai ƙarfi a diflomasiyya daga nahiyar da ke da muhimmanci sosai a duniya," in ji shi.