Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye dangane da muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya na ranar 27/03/2026

Rahoto kai-tsaye

Usman MINJIBIR, Abdullahi Bello Diginza da Isiyaku Muhammad

  1. Za mu ƙarƙare yaƙin Iran nan da wata ɗaya - Amurka

    Sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio, ya shaida wa taron ministocin harkokin wajen kasashe masu karfin tattalin arziki G-7 cewa za a ci gaba da yakin da Amurka ke yi da Iran na tsawon makonni biyu zuwa hudu.

    Da yake magana da manema labarai bayan taron, babban jami'in diflomasiyyar Amurkan ya ce zuwa wannan lokacin Amurka ta cike burukanta.

    Tun da farko dai ministocin harkokin wajen kasashen kungiyar sun fitar da wata sanarwa inda suka bukaci a sake bude mashigin Hormuz.

  2. Mataimakin gwamnan Kano Aminu Abdussalam ya yi murabus

    Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdussalam Gwarzo ya yi murabus daga muƙaminsa.

    Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da ƙungiyar Kwankwasiyya ta fitar, wadda kakakinta Dr Habibu Sale Mohammed ya fitar da yammacin ranar Juma'a.

    Ya ce mataimakin gwamnan ya É—auki matakin ne domin tabbatar da zaman lafiya a jihar Kano da tabbatar da ba a haifar da tsaiko a mulkin jihar ba.

    "Sai dai ya kamata a fahimci cewa ajiye aikin da ya yi, ba ya nufin ya amince da tuhume-tuhumen da majalisar dokokin jihar ke masa. Mataimakin gwamnan yana nan da gaskiyarsa. Kawai ya yi murabus ne domin fifita Kano da al'ummarta da kuma hana duk wani abu da zai iya barazana ga cigaban jihar."

    Sanarwar ta ƙara da cewa tsohon mataimakin gwamnan zai mayar da hankali ne wajen raya ƙungiyar Kwankwasiyya musamman domin fuskantar zaɓukan 2027.

  3. Mahaifiyar Nasir El-Rufai ta rasu

    Mahaifiyar tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai mai suna Hajiya Umma El-rufai ta rasu.

    ÆŠan tsohon gwamnan, Bello El-Rufai ne ya sanar da rasuwar a ranar Juma'a, inda ya rubuta a shafinsa na Facebook cewa, "Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un. Ina sanar da al'umma cewa Allah ya yi wa kakata, Hajiya Umma El-Rufai rasuwa," in ji shi.

    Marigayiyar ita ce mahaifiyar Malam Nasir El-Rufai. "Muna godiya ga Allah bisa rayuwar da ta yi. Muna addu'ar Allah ya jiƙanta da rahama. Muna buƙatar addu'arku a gare ta," in ji shi.

    Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da tsohon gwamnan ke tsare a hannun hukumar ICPC, inda ake ci gaba da gudanar da shari'a kan zarginsa da badaƙala a lokacin da yake gwamnan jihar Kaduna.

  4. Ba mu tura ƙarin dakaru Gabas ta Tsakiya ba - Amurka

    Ma'aikatar tsaron Amurka ta Pentagon ta musanta rahotonnin da ke cewa tana duba yiwuwar aika ƙarin dakaru yankin Gabas ta Tsakiya.

    Mujallar Walla Street Journal ta bayar da rahoton cewa ƙara yawan dakarun zai bai wa Donald Trump damar ƙarin zaɓi.

    Rundunar dakarun juyin ta fitar da sabon gargaÉ—in cewa mashigar Hormuz za ta ci gaba da kasancewa a rufe.

  5. Saudiyya ta ce ta kakkaɓo jirage marasa matuƙa da suka nufi Riyadh

    Ma'aikatar tsaron Saudiyya ta ce ta kakkaɓo wasu jirage marasa matuƙa guda uku da suka nufi yankin Riyadh.

    Ma'aikatar ta ce jiragen sun faɗo a kusa da wani sansanin soji ba tare da haifar da wata ɓarna ba.

  6. Iran ta hana wasu jirage wucewa ta mashigar Hormuz

    Dakarun juyin juy halin Iran sun ce sun hana wasu jiragen ruwa uku da suka yi ''yunƙurin wucewa ta mashigar Hormuz da safiyar yau Juma'a''.

    Rundunar ta IGRC ta ce jiragen uku na ƙasashe daban-daban sun yi yunƙurin wucewa ta wurin da aka yarje wa wasu wucewar, amma sai dakarun rundunar sojin ruwa ta IGRC ta mayar da su baya.

    Rundunar ta ce mashigar a rufe take kuma duk jirgin da ya yi yunƙurin wucewa ta mashigar zai gamu da fushinta.

    IGRC ta ce ta haramta wucewar duk wani jirgi na ƙasar da ke ƙawance da Amurka ko Isra'ila wucewa ta mashigar.

    Ministan harkokin wajen ƙasar, Abbas Araghchi ya bayyana ta gidan talbijin na ƙasar, kwana biyu da suka gabata cewa Iran ta samu buƙata a hukumance na buɗe mashigar daga wasu ƙasashen da suka haɗa da China da Rasha da Pakistan da Iraƙi da kuma Indiya.

    Ya bayyana cewa daga ɓangaren Iran, ba ta rufe mashigar duka ba, ya ce an rufe ta ne kawai da wadanda ya bayyana da ''maƙiya''.

  7. Fiye da wakilai 8,000 da gwamnonin APC 31 na shirin halartar taron APC

    Aƙalla wakilai 8,433 daga sassan Najeriya daban-daban ne tare da gwamnoni 31 ne ake sa ran za su halarci babban taron ƙasa na jam'iyyar APC mai mulkin ƙasar.

    Shugaban ƙasar Bola Tinubu da ministocinsa da ma gwamnonin jam'iyyar 31 ne za su jagoranci taron.

    Jam'iyyar za ta zaɓi shugabannin da za su jagorance nan da shekara huɗu masu zuwa.

    Tuni dai jam'iyyar ta sanar da aniyar amfani da hanyar masalaha wajen zaɓen sabin shugabannin nata.

    Cikin waɗanda ke takarar har da shugaban riƙon jam'iyyar na yanzu, wanda tuni aka tantance domin tsayawa takarar.

    Haka ma wasu bayanai na ambato tsohon gwamnan jihar Nasarawa, Tanko Almakura.

  8. Matar da ke son mutuwa da taimakon likitoci a Spain ta mutu

    Wata mata mai shekara 25 ta rasu ta hanyar kashe kanta da taimakon likitoci a ƙasar Spain, bayan shafe lokaci ana takaddama a kotu da mahaifinta wanda ya yi ƙoƙarin hana aiwatar da kisan.

    Gwamnatin yankin Catalonia ta bai wa Noelia Castillo damar yin hakan kusan shekaru biyu da suka gabata, amma sai aka dakatar da aiwatar da kisan bayan da aka shigar da ƙorafe-ƙorafe.

    An ce ta zama gurguwa ne sakamakon raunukan da ta samu lokacin da ta yi yunƙurin kashe kanta bayan an yi mata fyade.

    Ƙasar Spain ta halatta kashe kai da taimakon likitoci, tun shekaru biyar da suka gabata.

  9. Hare-harin Isra'ila sun kashe mutum 18 a Iran

    Aƙalla mutum 18 ne suka rasu a wani hari da Isra'ila ta kai da daddare a birnin Qom na ƙasar Iran.

    Kamfanonin dillancin labarai na Fars da Tasnim sun rawaito cewa harin ya faru a yankin Pardisan na birnin da safiyar ranar Juma'a inda aka fara samun mutuwar mutum shida kafin a samu ƙari.

    Kafafen sun ce mutum 10 sun samu raunuka.

    Ƙungiyar agajin gaggawa ta Red Crescent Society ta ce masu aikin ceto sun halarci wurin da abin ya afku wanda ta bayyana da unguwannin farar hula

  10. Jiragen ruwan Mexico sun ɓace a hanyarsu ta kai agaji Cuba

    Rundunar sojin ruwan Mexico ta ce tana neman wasu ƙananan jiragen ruwa guda biyu da suka ɓace yayin da suke ɗauke da kayan agaji zuwa ƙasar Cuba.

    Rundunar ta bayyana cewa jiragen sun tashi ne daga tsibirin Isla Mujeres da ke gabar tekun Kaebiyan a ranar 20 ga watan Maris, amma har yanzu ba su isa Havana kamar yadda aka tsara ba.

    Wakiliyar BBC ta ce jiragen na cikin wasu ayarin jiragen ruwa na taimakon kasa da kasa da jama’a ke aikawa domin kai kayan abinci da magunguna zuwa Cuba.

    Yanzu haka dai mutane a kasar na fama da yawan katsewar wutar lantarki da kuma tabarbarewar tattalin arziki, lamarin da ake dangantawa da takunkumin man fetur da Amurka ta kakabawa kasar da nufin kifar da gwamnatin da ba ta ga maciji da ita.

  11. Iran ta shawarci mazauna kusa da sansanonin Amurka su tashi

    Rundunar juyin juya hali ta ƙasar Iran, IRGC ta gargaɗi al'ummar da ke zaune kusa da sansanonin sojin Amurka a dukkannin yankin Gabas ta Tsakiya da su bar wurin.

    A wata sanarwa da IRGC ta fitar ta hannun kamfanin dillancin labarai na Fars News ta soki Amurka da Isra'ila da "fakewa da amfani da fararen hula", inda kuma sanarwar ta ƙara zargin Amurka da Isra'ila da kisan fararen hula da jami'an gwamnatin Iran.

    Wannan dai na zuwa a daidai lokacin da shugaban Amurka, Donald Trump yake iƙrarin ƙasarsa da Isra'ila na tattaunawa da Iran kan yadda za a cimma tsagaita wuta.

    Iran dai ta sha fitowa ta musanta ikrarin na Amurka inda jami'an rundunar juyin juya halin na Iran ke cewa "Trump na tattaunawa da kansa" ne.

  12. Saudiyya da Kuwait sun fuskanci hare-haren makamai masu linzami

    Aƙalla makamai masu linzami shida ne da aka aike da su zuwa yankin Riyadh na Saudiyya, ƙasar ta ce ba su samu nasarar harar ko'ina ba.

    Ma'aikatar tsaron Saudiyya ta ce ta samu nasarar kakkaɓo makaman guda biyu sannan guda huɗu sun faɗa cikin ruwa.

    Ita ma Kuwait ta rawaito hare-haren da safiyar ranar Juma'a.

  13. Ƴan majalisar Birtaniya na son a rage dogaro da Amurka kan tsaro

    Wasu ‘yan majalisar dokokin Birtaniya da takwarorinsu na Turai, sun yi gargadin cewa dole ne ƙasar ta rage dogaro da Amurka wajen tsaro.

    Wani rahoto da kwamitin majalisar kan dabarun tsaron kasa ya fitar ya ce kamata ya yi Birtaniya ta fara shirin lokacin da za a tsinci kai a wani yaanayi da Amurka za ta tsame kanta daga duk wani abu da ya shaif kulawa da Turai da taimaka wa nahiyar wajen kare kanta sa'ad da aka shiga matsala.

    Rahoton ya ce ba laifi bane a ci gaba da hadin gwiwa da Amurka a fannonin da suka dace, amma ya jaddada cewa dole ne kasashen nahiyar su farga, su bijiro da wani sabon tsari da zai kare su baki daya.

    Wannan na faruwa ne yayin da a baya bayan nan ake samun tabarbarewar dangantaka tsakanin gwamnatin shugaba Trumo na Amurkar da kasashen Turai da kuma mambobin NATO dangane da shiga yakin Ukraine.

  14. Abin da Trump ya ce kan tattaunawa da Iran

    Shugaban Amurka Donald Trum ya ce ya dakata da kai wa cibiyoyin makamashin Iran har zuwa nan da kwanaki 10 saboda tattaunawar da ake yi da Tehran kamar yadda ya yi iƙrari.

    Bayanin nasa na zuwa ne bayan taron majalisar ministoci a fadar White House ranar Alhamis - irinsa na farko tun fara yaƙi da Iran. Ga wasu muhimman abubuwan da ya faɗa:

    • Amurka ta share sojojin ruwa da na sama na Æ™asar Iran "gabaÉ—aya" sannan lalata kusan kaso 90 na makamai masu linzamin Æ™asar.
    • Ya kuma ce Iran na rokon a cimma tattaunawa kuma Amurka za ta ci gaba da kashe su idan har Iran É—in ta Æ™i aminicewa da tattaunawar. Ya kuma bayyana sojojin Iran da "ragwage amma sun iya neman sulhu da tattaunawa."
    • Jakadan Amurka na musamman, Steve Witkoff, wanda shi ma yana wurin taron ya ce Amurka ta aike da daftari mai buÆ™atu 15 ga Iran ta hannun Pakistan.
    • Trump ya ce idan Iran ta Æ™i amincewa da tsagaita wuta, Amurka za ta kasance "babbar dodo" gare ta, inda ya Æ™ara da cewa " za mu ci gaba da kawar da su ne kawai".

    Kasar Iran dai ta sha faɗin cewa ita ba ta nemi tattaunawa ba kuma ma ba za ta amince da tsagaita wuta ba sai dai dakatar da yaƙi baki ɗayansa. Bugu da ƙari, Iran ta fitar da wasu buƙatu guda biyar da ta ce su ne sharuɗɗan dakatar da yaƙi.

  15. 'Ana gab da fara tattaunawa tsakanin Amurka da Iran'

    Ministan harkokin wajen Jamus, Johann Wadephul ya ce wakilai daga Amurka da Iran na shirin haÉ—uwa domin fara tattaunawa a Pakistan, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito.

    Da yake magana da gidan rediyo na Deutschlandfunk, Wadephul ya ce "akwai tattaunawar da ba ta gaba da gaba ba" tsakanin ƙasashen guda biyu sannan "an yi shirin sake ganawa domin tattaunawa ta gaba da gaba," wanda ya yi imanin za a yi ta "ba da jimawa ba a Pakistan."

  16. Amurka na ganawa da kungiyar G7

    Sakataren harkokin wajen Amurka ya isa birnin Paris domin halartar taron ƙasashen G7.

    Ana sa ran Marco Rubio zai fuskanci matsin lamba daga sauran ƙasashen domin kawo karshen rikicin Gabas ta Tsakiya.

    Ƙasashen G7 na nuna damuwa kan tasirin rikicin musamman kan farashin mai da tattalin arzikin duniya, tare da fargabar kada lamarin ya sake dagulewa.

    Za a buƙaci Mista Rubio ya fayyace matsayar Washington da kuma ainihin halin da ake ciki dangane da tattaunawar da ake yi da Iran.

    Haka kuma, sauran ƙasashen kungiyar za su matsa wa Amurka lamba kada ta manta da batun Ukraine.

    Babbar jami’ar harkokin manufofin Turan, Kaja Kallas, wadda ke halartar taron, ta ce akwai alaƙa a bayyane tsakanin rikice-rikicen biyu, tana mai cewa Moscow na bai wa Tehran tallafi.

  17. Trump ya ƙara tsawaita lokacin kai harehare kan cibiyoyin makamashin Iran

    Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce zai ƙara jinkirta barazanar da ya yi ta fara kai hari kan cibiyoyin makamashin Iran da wasu kwanaki goma.

    A wani saƙo da ya wallafa a shafukan sada zumunta, ya ce an ɗauki matakin ne bisa buƙatar Iran, yana mai jaddada cewa cewa tattaunawar da ake yi da ƙasar na tafiya yadda ya kamata.

    Sai dai a na ta ɓangaren Iran ta ce babu wata tattaunawa kai tsaye da ake yi, amma wakilin Trump din Steve Witkoff na aika masu sakonni ta bayan fage ta hannun Pakistan da ke shiga tsakani.

    Shugaba Trump ya ki bayyana dalilin da ya sa a gefe guda gwamnatinsa ke ta tura ƙarin sojoji zuwa yankin, sai dai ya yi gargaɗin cewa Iran ɗin za ta ɗanɗana kuɗarta, idan har ta ƙi amincewa da buƙatunsa.

  18. BuÉ—ewa

    Masu bibiyarmu barkan ku da warhaka barka da sake saduwa a cikin wani sabon shirin shafin kai tsaye na BBC Hausa da ke kawo muku bayanai da rahotanni dangane da muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Da fatan za ku ci gaba da kasancewa da shafin na kai tsaye da ma sauran shafukan sada zumunta na BBC Hausa.

Trending Now