, Daga Jaridu
Liverpool ce kan gaba a neman siyen ɗan wasan Bournemouth da Argentina,Marcos Sensi, da kwantaraginsa zai ƙare a wannan kaka. (i paper)
Manchester City na dab da kamala tayin siyen ɗan wasan Feyenoord Givairo Read, sai dai Bayern Munich ita ma na harin ɗan wasan. (Sky Sports)
Livepool na son ɗauko ɗan wasan Newcastle Anthony Gordon, da ɗan wasan Everton Iliman Ndiaye, a yunƙurinsu na ƙara inganta ƴan wasan gaban ƙungiyar a kaka mai zuwa. (Teamtalk)
Tsohon ɗmai horar da Chelsea da Manchester United, Jose Mourinho na kan gaba cikin wanda Newcastle ke son ya maye gurbin Eddie Howe, idan har suka yanke shawarar sallamar mai horar da ƴan wasan ƙungiyar. (Talksport)
Bournemouth na mataki na gaba wajen ɗaukar tsohon mai horar da ƴan wasan Borussia Dortmund da RB Leipzig Marco Rose, kasancewar ba ya tare da wata ƙungiyar a halin yanzu. (Telegraph - subscription required)