Benjamin Netanyahu ya umarci ministocinsa da su fara tattaunawa da Lebanon
Firayim Ministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce ya umurci majalisar ministocinsa da su fara tattaunawar kai tsaye da gwamnatin Lebanon cikin gaggawa.
Sanarwar ta zo ne jim kaɗan bayan da sojojin Isra'ila suka fitar da wani sabon gargaɗi na ficewa ga mazauna yankunan kudancin babban birnin ƙasar Lebanon.
Dakarun sojin Isra’ilar dai sun ce sun kai hari wuraren da kungiyar Hezbollah ke amfani da shi wajen kai hare-hare a Lebanon.
Wannan na zuwa ne ba da jimawa ba, bayan Benjamin Netanyahu ya ce ya umarci majalisar ministocinsa da su fara tattaunawa kai tsaye da gwamnatin Lebanon cikin gaggawa.
Wakilin BBC ya ce Mista Netanyahu ya ce tattaunawar za ta mayar da hankali kan kwance damarar Hezbollah da kuma kafa dangantaka ta zaman lafiya.
Sai dai Isra’ila ta fuskanci suka sosai saboda hare-haren da ta kai a jiya Laraba, inda ma’aikatar lafiya ta Lebanon ta ce mutane fiye da ɗari uku ne suka rasa rayukansu.
Wani jami’in Lebanon ya ce gwamnatinsu na son a cimma tsagaita wuta kafin fara kowace irin tattaunawa da Isra’ila.