Iran ta bayyana wa Pakistan matsayinta kan kawo ƙarshen yaƙin ƙasar
Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya fitar da wata sanarwa bayan ganawarsa da babban hafsan sojin Pakistan, Asim Munir.
Sanarwar ta bayyana cewa sun tattauna ''batutuwa masu muhimmanci dangane da yarjejeniyar tsagaita wutar'' tsakanin Iran da Amurka.
Haka ma sanarwar ta ce Araghchi ya bayyana wa Pakistan matsayinta da shawarwarinta kan kawo ƙarshen yaƙin.
Sanarwar ta ƙara da cewa Asim Munir ya ce Pakistan a shirye take ta ci gaba da aikinta na shiga tsakani.