Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 23/02/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin 23 ga watan Maris 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Abdullahi Bello Diginza

  1. Jawabin Trump kan harin cibiyoyin makamashin Iran ya motsa farashin mai

    Farashin man fatur ya sauka sosai bayan jawabin Shugaba Trump kan yaƙin Iran. Farashin ya sauka ne da kusan kashi 10 na asalin farashin mai samfurin Brent, duk da ya ɗan ƙara tashi, inda a yanzu haka ake hada-hadar gangar man a kusan dala 100.

    Haka kuma kasuwannin jarin turai ma sun ɗan motsa, inda ma'aunin kasuwar jarin Jamus na Dax ya samu tagomashi bayan a baya ya karye da sama da kashi biyu.

    Ministan harkokin wajen Singapore ya bayyana wa Reuters cewa yaƙin ya jefa tattalin arzikin duniya cikin halin ha u la i.

  2. Hare-haren Isra'ila sun karya gada ta biyu a tekun Litani na Lebanon

    Kafofin yada labaran kasar Labanon sun ruwaito cewa an kai hari kan gada ta biyu da ta tsallaka kogin Litani a kudancin kasar.

    Hakan na zuwa ne bayan umurnin da majalisar kula da harkokin yaki ta Isra'ila ta bai wa sojoji a ranar Lahadin da ta gabata da su zafafa kai hare-hare kan gadoji a kan kogin.

    Isra'ila ta ce ana amfani da su wajen ayyukan ta'addanci. An kaddamar da wani hari kan wata babbar gada a ranar Lahadin da ta gabata, lamarin da shugaban kasar Labanon Joseph Aoun ya yi Allah-wadai da shi da kuma duk wani hari kan ababen more rayuwa, kuma ya bayyana a matsayin ta'azzarar yakin mai cike da hadari.

    Ya kara da cewa kai hari ga gadojin kogin Litani zai kawo cikas wajen kai kayan agaji.

  3. Ƴanbindiga sun fasa gadoji biyu a Neja domin taƙaita aikin jami'an tsaro

    Hukumomi a jihar Neja da ke Najeriya sun ce wasu mutanen da ake zargin masu tayar da kayar baya ne sun fasa wasu gadoji a jihar. Yayin da wata motar fasinja ta taka wani abu mai fashewa, lamarin da ya janyo jikkatan mutane.

    Jihar ta Neja na daga cikin jihohin da suka jima suna fuskantar matsalar tsaro, musamman wadda ta shafi ayyukan ƴan fashin daji.

    Ƴanbindigar sun yi amfani da bom ne, inda suka tarwatsa gadar da ke hanyar Luma a ƙaramar hukumar Borgu, sannan suka jefa bom a wata gadar, amma ita ba ta tarwatse baki ɗaya ba.

    Sakataren gwamnatin jihar Neja, Abubakar Usman ya tabbatar da aukuwar lamarin a zantawarsa da BBC Hausa, inda ya ce maharan sun jefa bama-baman ne a gadojin da sanyin safiyar yau Litinin.

    Haka rahotanni na nuna cewa wata motar fasinja ta taka wani bom a titin Nuku zuwa Woro, inda fasinjojin baki ɗaya suka mutu.

    "Tabbas manufarsu ke nan su hana jami'an tsaro tsallakawa. Suna so su yi cikas kan ayyukan sojoji ne a yankin," in ji shi.

    Ko a jihar kwara da ke tsakiyar kasar ma, an samu mutuwar wani direba a yau bayan motar da yake ciki ta taka bam.

  4. Gobe Talata ICPC za ta gurfanar da El-Rufai a kotu a Kaduna

    Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta ICPC ta sanar da shirinta na gurfanar da tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, a gaban kotu a ranar Talata 24 ga Maris, 2026.

    Hukumar ta ce za ta gurfanar da shi tare da wani Joel Adoga a Babbar Kotun Tarayya da ke Kaduna.

    A cewar sanarwar da ICPC ta fitar a ranar Litinin, ƙarar da ake yi wa El-Rufai ta ƙunshi tuhume-tuhumen da suka hada da karkatar da kadarorin gwamnati da mallakar kadarorin jama’a ba bisa ƙa’ida ba, da kuma halsata kuɗin haram. Hukumar ta ce an shigar da karar ne domin a bi diddigin zargin da ake yi.

    Haka kuma, ICPC ta bayyana cewa akwai wata ƙara ta daban da aka shigar a Babbar Kotun Jihar wadda ta shafi El-Rufai da wani Amadu Sule.

    A cikin wannan ƙarar, ana zarginsu da amfani da mukami ba daidai ba da damfara, yunƙurin aikata damfara, da kuma bai wa wasu gata ba bisa ka’ida ba.

    Hukumar ta ce an shigar da duka ƙararrakin biyu ne a ranar 18 ga Maris, 2026, kuma an riga an miƙa wa El-Rufai sammaci yadda ya kamata.

  5. El-Rufai ya cancanci kyautatawa saboda rawar da ya taka a mayar da mulki kudu - MURIC

    Ƙungiyar kare muradun Musulmi a Najeriya MURIC ta bayyana cewa tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya taka muhimmiyar rawa wajen bai wa ‘yan Kudancin Najeriya damar samun shugabancin ƙasa saboda haka ya kamata a kyautata masa a halin da yake ciki yanzu.

    A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Litinin 23 ga Maris, 2026, ƙungiyar ta ce ta daɗe tana fafutukar ganin an samu shugaban ƙasa Musulmi daga yankin Yarbawa.

    Ta ce hakan ya samo asali ne daga yadda take ganin Musulmi a yankin ke fuskantar ƙalubale a fannin siyasa da zamantakewa.

    Kungiyar ta bayyana cewa tun daga shekarar 2021 ta fara kira da a bai wa Musulmin Yarbawa damar kai wa ga shugabancin ƙasa, inda daga baya ta haɗa kai da wasu ƙungiyoyi wajen tuntubar manyan ‘yan siyasa ciki har da Bola Ahmed Tinubu domin ya tsaya takarar shugaban ƙasa.

    Ta ce hakan ya sa suka nemi goyon bayan manyan ‘yan siyasa daga Arewa ciki har da El-Rufai.

    MURIC ta jaddada cewa goyon bayan da El-Rufai ya bayar ya taimaka matuka wajen hada kan Arewa domin marawa takarar Tinubu baya, musamman a lokacin da ake ce-ce-ku-ce kan inda shugabancin ƙasa zai dosa.

    Ta ƙara da cewa El-Rufai ya taka rawa wajen tabbatar da cewa mulki ya koma Kudanci bayan shekaru takwas na mulkin Arewa.

    Ƙungiyar ta nuna damuwa kan yadda ake tafiyar da shari’ar El-Rufai a yanzu, tana mai cewa lamarin yana da nasaba da siyasa ba shari’a kawai ba.

    Ta bukaci a yi masa adalci, tana mai cewa bai kamata a barsa a cikin hali mai wahala ba yayin da wasu ‘yan siyasa da ke da shari’o’i ke ci gaba da zirga-zirga cikin ‘yanci.

  6. ‘Trump bai da tabbas’: Martanin Iraniyawa kan ɗage harin da ya yi

    Iraniyawa sun mayar da martani kan kalaman shugaban Amurka wanda ya ce ya ɗage kai hari kan cibiyoyin lantarkin Iran da kwanaki biyar inda suka ce Trump ba ya da tabbas, yayin da wasu ke bayyana damuwa kan abin da ka iya biyo baya.

    Hakan na zuwa ne duk da katsewar intanet da gwamnati ta yi a ƙasar, inda wasu ke ci gaba da samun hanyoyin shiga intanet.

    Wani matashi a birnin Tehran ya bayyana cewa ƙarshen wannan lamari zai iya yin babban tasiri ga rayuwar al’ummar Iran, ko da kuwa rundunar juyin juya halin Iran ta ci gaba da wanzuwa ko kuma ta kai ga karshenta.

    Wata budurwa daga arewacin Iran ta ce Trump yana “rikita mana hankali”.

    “Na kira abokina gama da wannan kalaman na Trump, sai kawai muka yi dariya. Wace irin rayuwa ce muke yi haka?” in ji wani matashi daga Tehran.

    Haka kuma, wata matashiya daga Tehran ta ce “Trump ba ya da tabbas kwata-kwata. Ban san abin da zai faru ba.

  7. Iran ta musanta tattaunawa da Trump kan ɗage kai mata hari

    Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta ce babu wata tattaunawa da ke gudana tsakanin Iran da Amurka tana mai mayar da martani ga kalaman shugaba Donald Trump.

    Wannan na zuwa ne bayan Trump ya bayyana cewa ya yi “tattaunawa ta gaskiya" da Iran kan hanyoyin kawo ƙarshen rikicin Gabas ta Tsakiya

    Sai dai Iran ta ƙaryata wannan iƙirari, tana cewa kalaman shugaban Amurka wani yunƙuri ne na rage farashin makamashi da kuma neman ƙarin lokaci domin aiwatar da shirinsa na soji.

    Bayan Trump ya sanar a shafinsa na Truth Social cewa ya ɗage kai hari kan tashoshin wutar lantarki da kayan makamashin Iran da kwanaki biyar, farashin mai ya faɗi, yayin da kasuwannin kudi suka samu ƙarin darajar hannayen jari.

    Haka kuma, ma'aikatar tsaron Iran ta ce “hanya guda ɗaya da ƙawayenta za su iya wucewa ta mashigar Hormuz ita ce “hanyar haɗa kai da Iran.”

    Ta ce ba Iran ba ce ta fara wannan yaki, don haka duk wani kira na rage tashin hankali ya kamata a mayar da shi ga Washington.

  8. Trump ya ce ya ɗage kai wa cibiyoyin lantarkin Iran hari da kwana biyar

    Shugaban Amurka, Donald Trump ya ce ya bayar da umarnin ɗage duk hari kan tashoshin samar da lantarki da sauran kayan aikin makamashin Iran har nan dakwana biyar.

    Mista Trump ya ce ya ya yi “tattaunawa ta gaskiya da Iran kan “hanyoyin kawo ƙarshen rikicin Gabas ta Tsakiya da kuma yadda za a warware matsalar yaƙin.”

    Shugaban na Amurka ya kuma ce "bisa ga irin tattaunawar da aka yi cikin kwanaki biyu da suka gabata, ya umurci ma’aikatar tsaron Amurka ta dakatar da duk wani hari kan tashoshin wuta da makamashin Iran har na tsawon kwanaki biyar, muddin tattaunawar da ake yi ta ci gaba da samun nasara.

  9. 'Babu shaidar cewa Iran na harin Birtaniya'

    Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya ce babu wata “shaida” da ke nuna cewa Iran na nufin kai hari kan Birtaniya.

    A lokacin da aka tambaye shi ko Birtaniya na cikin wuraren da Iran ke hari bayan harbin makamai zuwa tsibirin Diego Garcia, Starmer ya ce gwamnati “kullum tana yin bincike don kare tsaron kanta kuma babu wata shaida cewa Iran na nufin kai hari.”

    Ya ƙara da cewa akwai buƙatar rage tashin hankali, yana mai cewa yana da muhimmanci a kare muradun Birtaniya da rayuka “ba tare da shiga yaƙin ba.”

    Iran har yanzu bata bayar da wani martani na hukuma kan rahotannin harbin makaman zuwa Diego Garcia ba.

    Tazarar daga mafi kusa daga Iran zuwa London tana fiye da kilomita 4,300.

  10. Duk wanda ke son wucewa ta Hormuz ya ba mu haɗin kai - Iran

    Ma'aikatar tsaron Iran ta ce “hanya guda ɗaya da ƙawayenta za su iya wucewa ta mashigar Hormuz ita ce “hanyar haɗa kai da Iran.”

    Cikin wata sanarwa da ma'aikatar ta fitar, wadda kuma kafofin labaran ƙasar suka wallafa ta ce "duk wani yunƙurin maƙiya na kai wa gaɓar teku ko tsibiran Iran hari, zai sa mu rufe duka hanyoyin zuwa gaɓar kowace ƙasa da ke yankin Tekun Fasha ta hanyar dasa nakiyoyi a duka gaɓoɓin''.

    Sanarwar ta ƙara da cewa matsawar aka kai mata hari to ''baya ga mashigar Hormuz da za mu rufe, za mu kulle duka ƙasashen yankin Gulf, kuma dole wanda ya kawo mana hari ya ɗauki alhakin hakan.''

  11. Ba mu rusa duka rundunonin hukumarmu ba - IGP

    Rundunar ƴansandan Najeriya ta musanta rahotannin da ke cewa Babban Sufeto Janar na ƴansanda, Olatunji Disu, ya bayar da umarnin rusa duka rundunonin hukuman ƴansanda na musamman a jihohin ƙasar ba.

    A cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Anthony Placid, ya fitar, rundunar ta bayyana cewa rahotannin sun jirkita umarnin da IGP ya bayar.

    Sanarwar ta ce wasu kafafen yaɗa labarai sun ruwaito cewa Sufeto Janar ɗin ya umarci a rusa rundunonin musamman na ƴansanda da dama a faɗin ƙasar nan take, amma rundunar ta jaddada cewa wannan bayani ba daidai ba ce.

    Rundunar ta ƙara da cewa, duk da damuwar jama’a kan yadda wasu daga cikin rundunonin ke aiki, IGP na ganin suna taka muhimmiyar rawa wajen yaƙi da aikata laifuka a Najeriya.

    “IGP, wanda ya riƙe muƙamai daban-daban a faɗin ƙasar nan ya damu da yawaitar rundunoni na musamman na ƴansanda, wanda hakan na rage yawan jami’an da ke aiki a ofisoshin ƴansanda, tare da haifar da matsalolin da ke shafar martabar rundunar sakamakon wasu halaye marasa kyau na rundunonin da ba a kula da su sosai,” in ji sanarwar.

    A cewar rundunar, wannan mataki zai taimaka wajen ƙara yawan jami’ai a ofisoshin ’yan sanda, domin ƙarfafa aikin tsaro a matakin ƙasa da kuma magance koke-koken jama’a kan wasu ayyukan da suka wuce gona da iri daga rundunonin musamman.

  12. Hezbollah ta ce ta kai hare-hare fiye da 60 kan Isra’ila a rana guda

    Ƙungiyar Hezbollah ta ƙasar Lebanon ta ce ta kai hare-hare guda 63 kan Isra’ila a ranar Lahadi.

    A cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na Telegram, Hezbollah ta bayyana cewa ta yi amfani da makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa, da kuma harbin manyan bindigogi wajen kai hare-haren kan sojojin Isra’ila, a cikin Isra’ila da kuma kudancin Lebanon.

    Dangane da barazanar da Hezbollah ke yi, Isra’ila ta ƙaddamar da farmakin ƙasa a kudancin Lebanon.

    Tun daga ranar 1 ga watan Maris, hare-haren Isra’ila a Lebanon sun yi sanadin mutuwar mutane 1,029, tare da jikkata 2,786, yayin da sama da mutum miliyan guda suka rasa matsugunansu.

  13. Iran ta sake harba makamai masu linzami zuwa Isra’ila — IDF

    Rundunar sojin Isra’ila IDF, ta bayyana a sabon rahotonta cewa Iran ta harba makamai masu linzami zuwa ƙasar.

    A cewar rundunar, dakarunta na ci gaba da tare waɗannan hare-hare tare da kakkaɓo su kafin su kai ga wuraren da ake niyya.

    Tun da farko, rahotanni sun nuna cewa an ji ƙarar fashewar abubuwa a wurare da dama a babban birnin Iran, Tehran.

    Haka kuma, an ce an dakile wani sabon jerin hare-haren Iran a birnin Tel Aviv a cikin dare.

  14. Ba za mu bari matsalar tsaro ta durƙusar da ƙoƙarinmu ba - Tinubu

    Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa ba za ta bari matsalar tsaro ta durƙusar da ƙoƙarin da take yi na magance matsalar tsaro a sassan ƙasar daban-daban tare da tabbatar da inganta tsaro da walwalar ƴan ƙasar

    Shugaban ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi a lokacin da mataimakinsa da ƙungiyar gwamnonin ƙasar suka kai masa ziyarar gaisuwar sallah a gidansa da ke Legas.

    Tinubu ya ce "tattaunawar da na yi a lokacin ziyarar aiki da na kai Birtaniya ta mayar da hankali ne kan tsaro da jin daɗin al’umma, tare da nemo hanyoyin samun kayan aiki da tallafi daga ƙasashen waje."

    Tinubu ya ƙara da cewa ya tattauna da shugaban ƙasar Faransa Emmanuel Macron kan haɗin gwiwa wajen samar da kayan tsaro da tallafi.

    Ya ce "gwamnati na ƙoƙarin ƙarfafa alaƙa da sauran ƙasashe domin inganta tsaro, yana mai bayyana cewa rashin tsaro babbar barazana ce ga ci gaba da walwalar ƙasa.

    Haka kuma shugaban ya yi gargaɗin tasirin rikicin Gabas ta Tsakiya kan tattalin arziƙin ƙasa, musamman hauhawar farashin man fetur da rage ƙarfin saye.

    Tinubu ya kuma buƙaci gwamnonin su ƙirƙiri matakan rage raɗaɗin wannan matsala ta hauhawar farashin man fetur ga al’umma, musamman a fannoni kamar makamashi da sufuri, tare da ƙara tallafawa marasa ƙarfi.

    A nasa jawabin, shugaban ƙungiyar gwamnonin Najeriya kuma gwamnan jihar Kwara AbdulRahman AbdulRazaq ya yaba da ƙoƙarin shugaban ƙasa, yana mai cewa gwamnonin za su ci gaba da aiki tare domin kawo ƙarshen matsalar tsaro.

    Ya kuma bayyana cewa ana ci gaba da tattaunawa kan batun ‘yan sandan jihohi, tare da shirin kai batun gaban majalisar dokoki domin samar da doka mai ɗorewa.

  15. Saudiyya ta ce ta kakkaɓo jiragen marasa matuƙa biyu da makami mai linzami

    Ma’aikatar tsaron ƙasar Saudiyya ta sanar da cewa dakarun tsaron sararin samanta sun kakkaɓo tare da lalata jirage marasa matuƙa guda biyu a yankin Gabashin ƙasar.

    A cikin awa guda kafin haka, jami’an tsaron sun kuma kakkabo wani jirgin mara matuƙi a yankin, tare da daƙile wani makami mai linzami da aka harba zuwa birnin Riyadh.

  16. 'Yaƙin Iran da Amurka da Isra’ila ya jawo matsalar mai mafi muni a Gabas ta Tsakiya'

    Shugaban hukumar kula da nukiliya ta duniya ya ce yaƙin da Amurka da Isra'ila ke yi da Iran ya haifar da matsalar mai a Gabas ta Tsakiya - matsalar da ta fi wadda ta faru sau biyu a shekarun 1970, haɗi da wadda yaƙin Rasha da Ukraine ya haifar, gaba daya.

    Fatih Birol ya gaya wa manema labarai a babban birnin Australia, Canberra, cewa aƙalla ƙadarorin makamashi arba'in ne a fadin ƙasashe tara - ko dai matsalar ta lalata ko kuma ma ta yi musu mummunar illa sosai.

    Shugaban hukumar nukiliyan ya yi gargaɗin cewa matsalar da aka samu ta wucewa da mai ta mashigar Hormuz za ta shafi tattalin arziƙin duniya musamman ma Asia.

    Shugaban na IAEA, ya ce, har yanzu ba a fahimci illar tasirin hakan ba sosai a Turai, kuma babbar hanya daya ta magance matsalar ita ce bude mashigar Hormuz.

  17. Isra'ila ta ce tana ƙaddamar da sababbin hare-hare a babbann birnin Iran, Tehran

    Rundunar sojin Isra'ila ta ce tana ƙaddamar da wasu sababbin hare-hare a babbann birnin Iran, Tehran.

    Kafofin yaɗa labarai na Iran sun bayar da rahotannin fashewa a wurare daban-daban a Tehran din.

    Tun da farko Iran dai ta harba makamai masu linzami a kan Isra'ila, inda aka riƙa jin ƙarar jiniya ta ankararwa a arewaci da tsakiyar, Isra'ilar.

    Makamai masu 'ya'ya da sauran tarkacen bam sun yi illa a wurare da yawa a tsakiyar Isra'ila - amma kuma babu rahoton jikkatar mutane.

    Iran ta yi gargadin cewa za ta rufe mashigar Hormuz gaba daya muddin Amurka ta aiwatar da barazanar Shugaba Trump ta cewa zai shafe gaba dayan tasoshin samar da lantarki na Iran

  18. Za mu mayar da martani daidai da irin barazanar da aka yi mana - Iran

    Iran ta ce za ta mayar da martani ga duk wata barazana daidai da irin tasirin da take da shi domin kare kanta, kamar yadda rundunar juyin juya halin Iran IRGC ta bayyana a cikin wata sanarwa.

    Wannan na zuwa ne bayan barazanar da shugaban Amurka, Donald Trump ya yi na kai hari kan tashoshin wutar lantarkin Iran, tana mai cewa hakan zai kawo tsaiko ga ayyukan jin ƙai kamar asibitoci da cibiyoyin agaji da hanyoyin samar da ruwa da kuma cibiyoyin tace ruwa.

    Sanarwar ta ƙara da cewa idan aka kai hari kan tashoshin wutar lantarkin Iran, to Iran za ta mayar da martani ta hanyar kai hari kan tashoshin wutar lantarkin ƙasashen yankin da ke samar da wuta ga sansanonin Amurka

    Haka kuma za su kai hari kan cibiyoyin tattalin arziki da masana’antu da makamashi da Amurkawa ke da hannu a ciki.

    A cewar IRGC: “Kun kai hari kan asibitocinmu, ba mu mayar da martani ba. Kun kai hari kan cibiyoyin agaji, ba mu mayar ba. Kun kai hari kan makarantunmu, ba mu mayar ba. Amma idan kun kai hari kan wutar lantarki, mu ma za mu kai hari kan wutar lantarki.”

    Rundunar ta kuma musanta zargin da Donald Trump ya yi na cewa Iran na shirin kai hari kan cibiyoyin tace ruwan gishiri.

    Sanarwar ta ce sojojin Amurka sun kai hare-hare kan cibiyoyin samar da ruwa guda biyar, ciki har da cibiyar tace ruwa ta tsibirin Qeshm, amma IRGC ba ta taba kai irin wannan hari ba.

    Saboda haka ne Iran ta ce za ta mayar da martani ga duk wata barazana daidai da irin tasirin da take da shi.

  19. Yaƙin Iran – Ƙasashen da ke ƙirga riba da waɗanda ke tafka asara

    Tun daga hauhawar farashin mai da gidaje a Yorkshire ya zuwa rufe makarantu saboda tsadar abin hawa a Pakistan, babu wanda b yai ji a jikinsa game da yaƙin da ake yi a Gabas ta Tsakiya.

    A bayyane take cewa ramuwar gayya da Iran ta ƙaddamar, ya yi matuƙar tasiri wajen wargaza tsarin tattalin arziƙi da yin lahani, sai dai komai zai iya wucewa.

    Amma tabbas ba abu ne da aka saba gani ba.

    Sai dai duka wahalar da yaƙin ya jefa duniya a ciki, akwai waɗanda su kuma riba suke ƙirgawa sakamakon yaƙin.

    Masu cin riba: Norway, Canada da Rasha

    Duk da ƙoƙarin da duniya ke yi na mallakar makamashin da ba ya gurɓata muhalli, har yanzu duniya ta fi dogaro kan man fetur da iskar gas.

    Don haka ga masu rumbunan waɗannan makamashi, tamkar ɗimbin dukiya ce gare su, musamman yadda ake kallon man fetur a matsayin ''baƙin zinare''.

  20. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Litinin daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Aisha Babangida ke fatan kasancewa da ku a dai-dai wannan lokacin.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.

Trending Now