'Mun kai wa kamfanin sarrafa sinadaran man fetur na Amurka a Saudiyya hari'

Asalin hoton, Getty Images
Dakarun juyin juya hali Iran sun ce sun kai hari kan manyan kamfanonin sarrafa sinadaran man fetur mallakin Amurka da ke Saudiyya, ciki har da cibiyoyi a yankin Jubail da Al-Juaimah, a matsayin martani ga harin da aka kai kan masana’antar Asaluyeh.
Sanarwar ta ce a jerin hare-haren Iran karo na 99”, an kai hare-hare da makamai masu linzami da jiragen yaki marasa matuki kan sansanonin Amurka da kadarorinta a yankin Tekun Farisa da mashigar Hormuz, da kuma cibiyoyin tsara kai hare-hare a Isra’ila.
Dakarun sun bayyana cewa harin na zuwa ne a matsayin ramuwar gayya kan abin da suka kira hari kan “ kamfanin sarrafa sinadaran man fetur da ke Asaluyeh”.
Sun ƙara da cewa a matakin farko na harin, sun nufi manyan cibiyoyin sarrafa sinadaran man fetur da suka hada da na kamfanonin Amurka irin su ExxonMobil da Dow Chemical Company da kuma Chevron Phillips Chemical, inda aka ce an kai musu hari da makamai masu linzami.
Har ila yau, dakarun sun yi gargaɗin cewa idan sojojin Amurka suka tsallake iyakar da suka gindaya, martanin da za su mayar zai wuce yankin Gabas ta Tsakiya.
Sanarwar ta ce za su yi aiki kan lalata cibiyoyin samar da mai da iskar gas na Amurka da kawayenta domin hana su anfani da albarkatun yankin na tsawon shekaru.
Sun kuma gargadi kawayen Amurka a yankin da cewa a baya sun nuna hakuri saboda kyakkyawar makwabtaka, amma yanzu sun cire duk wani sharadi wajen zabar wuraren da za su kai hari.
Dakarun sun ƙara da cewa ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen kai hare-hare har ma da wuraren fararen hula idan rikicin ya ƙara ƙamari.












