Sabon jagoran addinin Iran ya sake fitar da saƙo

Asalin hoton, Tasnim News Agency
Kafofin yaɗa labaran Iran sun wallafa wata rubutacciyar wasiƙa da suka ce sabon jagoran addinin ƙasar, Mojtaba Khamenei ne ya aika da ita.
Cikin wasiƙar da aka aika a yau da ake gudanar da bikin Ranar Soji ta Iran, jagodan addainin bai ambaci manyan abubuwa biyu da jami'an Iran ke tattaunawa a kan a baya-bayan nan ba, wato batun mashigar Hormuz da yarjejeniyar dakatar da yaƙi da Amurka.
A wani ɓangare na wasiƙar Mojtaba Khamenei ya gargaɗi waɗanda ya kira ''maƙiya'' cewa sojojin Iran a shirye suke wajen sanya su ''ɗanɗanar ɗacin rashin nasara'', sai dai bai yi ƙarin haske game da hakan ba.
A baya ma jagoran addinin yakan fitar da irin waɗannan rubutattun saƙonni.
Tun bayan da aka naɗa shi jagoran addinin Iran a farkon watan Maris, Mojtaba Khamenei bai bayyana a bainar jama'a ba.





