Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye dangane da muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya na ranar 26/03/2026

Rahoto kai-tsaye

Usman MINJIBIR

  1. Sheikh Abduljabbar ya buƙaci sa bakin babban alƙalin Najeriya a shari'arsa

    Sheikh Abduljabbar Kabara ya yi kira ga babban alƙalin Najeriya da ya shiga lamarin shari'ar da yake da gwamnatin Kano.

    Malamin addinin musuluncin ya bayyana haka ne a wata wasiƙar ƙorafi da ya rubuta zuwa ga babban alƙalin, inda ya yi zargin ana jan ƙafa da gangan bayan ɗaukaka ƙara da ya yi kan hukuncin kisa da aka yanke masa bisa zarginsa da ɓatanci ga Annabi Muhammadu.

    A wasiƙar, ya yi ƙorafe-ƙorafe da suka haɗa da jan ƙafa da gangan hana shi samun cikakken bayanan shari'ar da zargin rashin daidaito da nuna son kai.

    Haka kuma ya yi zargin ba a yi masa adalci a shari'ar, sannan ya dasa alamar tambaya da shakku kan ikon da kotun shari'ar ke da shi na sauraron ƙarar tun a farko.

    A watan Disamban 2022 ne kotun shari'ar musulunci a Kano ta yanke wa malamin hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samunsa da laifin ɓatanci ga Annabi a cikin wa'azinsa.

    Bayan hukuncin ne malamin ya ɗaukaka ƙara, inda ya bayyana cewa ba a masa adalci a ƙaramar kotun ba, sannan ya ce ba a ba shi damar bayyana nasa ɓangaren ba, inda ya ƙara da cewa kalaman da ake magana daga littafai ya karanta su, kuma bai karanta da nufin cin mutunci ko ɓatanci ga Annabi ba.

    Ya ƙara da cewa bai aikata laifi ba, sannan ya ce idan har za a saurara shari'ar da adalci, yana da yaƙinin za a fahimce shi, kuma a wanke shi.

  2. 'Faransa ta janye gayyatar da ta yi wa Afirka ta Kudu zuwa taron G7'

    Afirka ta Kudu ta ce Faransa ta janye gayyatar da ta yi mata zuwa taron shugabannin ƙungiyar kasashe mafiya ƙarfin tattalin arziki a duniya wato G7 da za a yi a watan Yuni, saboda matsin lambar da Amurka ta yi mata.

    Kakakin fadar shugaban kasar ya ce an shaida musu cewa Faransa ta fuskanci matsin lamba na janye gayyatar da ta yi wa shugaba Cyril Ramaphosa, inda Amurka ta yi barazanar kauracewa taron idan ba a yi hakan ba.

    Shugaba Trump ya sha sukar gwamnatin Afirka ta Kudu a bainar jama'a, da sanya mata haraji mai yawa tare da caccakar Mista Ramaphosa kan zargin da ake yi na yi wa fararen fata 'kisan kare dangi' a kasar.

    Ministocin harkokin wajen kasashen G7 za su gana a Faransa a yau, domin tattauna muhimman matsalolin da duniya ke fuskanta, da suka hada da rikicin Iran da Ukraine.

  3. Iran ta ba jiragenmu izinin wucewa ta Mashigar Hormuz - Firaministan Malaysia

    Firaministan Malaysia, Anwar Ibrahim, ya bayyana cewa bayan tattaunawa da jami’an Iran, an ba jiragen ruwan ƙasarsa izinin wucewa ta Mashigar Hormuz.

    Ya ƙara da cewa ya gudanar da ganawar ne da ƙasashen Iran da Masar da Turkiyya da sauran ƙasashen yankin domin cimma wannan matsaya.

    Malaysia ta zama sabuwar ƙasa da ta sanar da cewa jiragenta za su rika wucewa ta wannan mashigar.

    Tun da farko, jiragen ruwan ƙasashen Koriya ta Kudu da Indiya da China da Japan sun riga sun samu damar wucewa ta wannan muhimmiyar hanyar ruwa.

  4. Ƙungiyar lafiya ta zargi RSF da tilasta wa aƙalla mutum 3,000 barin gidajensu

    Wata kungiyar lafiya ta Sudan ta zargi mayakan ‘yan tawayen RSF da tilstawa fiye da mutum 3,000 yin gudun ijira daga garuruwansu, tare da kai munanan hare-haren da suka lalata cibiyoyin kiyyon lafiya a jihar Bleu Nile.

    Mayakan na RSF dai sun kai hare-haren a wadannan cibiyoyi tare da kwashe magungunna da sauran muhimman kayan aiki.

    A cikin wani bayani da kungiyar likitocin ta Sudan ta fitar a ranar Laraba, ta ce mayakan na RSF sun farwa birnin Kumruk, kuma a lokaci guda suka kai hare-haren a asibitoci da cibiyoyin kiyyon lafiya tare da sace muhimman kayan aiki da suka hada da magungunna, bayan da cuka ci zarafin jami’an kiyyon lafiyar wadannan asibitoci wanda hakan ya yi sanadiyyar raunata mutum daya.

    Kungiyar likitocin ta kuma ce wadannan jerin hare-hare sun tilastawa dubban mazauna garuruwan da suka hada da mata da kananan yara yin kaura zuwa yankuna na kusa. Abin da ta bayyana da harin da mayakan na ‘yan tawayen RSF suka kitsa da gangan, kuma hakan ya jefa dubban mutanen cikin tsanani da tashin hankali kasancewar suna fuskantar karancin tallafin jinkai na gaggawa, tun ma ba na abinci da wuraren kwana da magungunna ba.

    Kazalaka, a cewar bayanin kai hari a cibiyoyin kiyyon lafiya da liktoci ya saba wa dokokin kare martabar fararen hula a duniya, da suka wajabta samar da kariya ga dukan asibitoci da cibiyoyin kiyyon lafiyar al’umma a lokacin yaki, to amma a kwanan nan RSF na matsa kaimi wajen kai farmaki a irin wadannan wurare a Sudan.

    Kasar Sudan ta soma fuskantar yakin na basasa tun a shakerar 2023, lokacin da rikici ya barke tsakanin dakarun sojin kasar da kuma na ‘yan tawayen na RFS.

    Rikicin mai nasaba da neman fadada karfin iko ya daidaita birane da garuruwa da dama a sassan na Sudan, musamman babban birnin kasar Khartoum, da kuma yammacin yankin Darfur.

    A wani rahoton Majalisar dunkin Duniya na baya-bayan nan ya nunar da cewa kimanin fararen hula 500 ne aka kashe tsakanin watannin Janairu zuwa tsakiyar Maris na wannan shekarar kasai, inda amfani da jirage marasa matuka wajen kai hare-hare a yankuna masu cin koson jama’a, ke kara jefa fargabar yadda makomar fararen hula za ta kasance.

    Kuniyar ta Likitocin Sudan ta nemi al’ummar duniya da kungiyoyin samar da jinkai su gaggauta daukar matakan samar da kayan agajin jinkai ga wadannnan al’umma da rikicin ya shafa.

  5. Kotu ta ba da umarnin kama shugaban PDP Tanimu Turaki

    Babbar Kotu a birnin tarayyar Najeriya Abuja, ta ba da umarnin kama shugaban tsagin jam'iyar PDP Tanimu Turaki.

    Jaridun ƙasar sun ruwaito cewa mai shari'a Peter Kekemeke, ya ba da umarnin ne bayan da Turaki ya ƙi bayyana a gaban kotun, domin bayar da bahasi kan wani zargi da Babban Sufetan ƴansandan ƙasar ya shigar a kan sa.

    A cikin ƙarar, rundunar ƴansandan ƙasar ta yi zargin cewa shugaban tsagin PDPn ya gabatar da bayanan ƙarya a wani ƙorafi da ya shigar a shekarar 2022.

    Mai shari'a Kekemeke, ya ce babu wata hujja da Turaki ya bayar na ƙin bayyana a gaban kotun, duk da cewa an sanar da shi.

    Kotun ta ba da umarnin a gabatar da shi a gaban kotun idan aka samu nasarar kama shi.

    Turaki ya riƙe muƙamin ministan ayyuka na musamman a gwamnatin tsohon shugaban ƙasar Goodluck Jonathan

  6. Google da Meta za su yi ƙarar Amurka kan neman su biya matashiya diyya

    Kamfanonin Google da Meta sun ce za su ɗaukaka ƙara kan hukuncin wata kotun Amurka da ta same su da laifi kan halin damuwar da wata matashiya ta shiga saboda tsananin amfani da manhajarsu.

    Masu taya alƙali yanke hukunci a Califonia sun nemi a biya matashiyar diyyar dala miliyan shida, saboda yadda ta zamo mai matuƙar amfani da Instagram da YouTube a lokacin ƙurucciyar ta.

    Ana sa ran hukuncin zai bayar da madogara kan dubban irinsa da ake jira a kotuna daban-daban na Amurka, ina ake zargin kamfanonin kafafen sadarwan da gazawa wajen kare masu amfamni da su.

  7. Hisbah ta kama wasu matasa a otel a Kano

    Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta ce ta kama wasu matasa 21 a wani otel da ke yankin Kureken Sani a ƙaramar hukumar Kumbotso bisa zargin aikata abubuwan da suka saɓa wa dokokin addini.

    Mataimakin Babban Kwamandan hukumar, Dakta Mujahid Aminuddeen, ya tabbatar wa jaridar Daily Trust faruwar lamarin, inda ya ce an kama mata 11, wasu daga cikinsu na da shekaru tsakanin 17 zuwa 25.

    Ya ƙara da cewa an kama maza 10, mafi yawansu matasa da shekarunsu ba su wuce 30 ba.

    A cewarsa, an cafke mutanen ne yayin da ake zargin suna shirya wani taro da ya saɓa wa dokokin Hisbah.

    Aminuddeen ya kuma bayyana cewa an kama manajan otel din dangane da wannan lamari.

    Ya ce za a gurfanar da waɗanda aka kama a gaban kotu domin fuskantar hukunci daidai da doka.

    Haka kuma, ya buƙaci al’umma da su riƙa sanya ido tare da kai rahoton duk wani abu da suke zargi, musamman wanda ya shafi kananan yara, ga hukumomin da suka dace.

    Wannan kamen na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan da hukumar ta sanar da kama matasa sama da 600 bisa zargin aikata abubuwan da ba su dace ba a lokacin bukukuwan Sallah da suka gabata.

  8. Isra'ila ta cire sunan Abbas Aragchi daga jerin mutanen da take son kashewa

    Wasu rahotannin da ke fitowa na cewa Isra'ila ta cire sunan ministan harkokin wajen Iran, Abbas Aragchi da kakakin majalisar dokokin kasar Mohammad Baqer Qalibaf daga jerin sunayen mutanen da za ta kai wa hari, bayan bukatar yin hakan daga jami'an Pakistan da Amurka.

    Wata majiyar tsaron Pakistan ta shaidawa kamfanin dillancin labaran Reuters cewa sun yi gargadin cewa kashe manyan jami'an biyu zai lalata kokarin da ake na cimma yarjejeniyar zaman lafiya.

    Kafofin yada labaran Amurka ma sun bayar da rahoton haka, suna ambato majiyoyi daga Amurka. Sai dai zuwa yanzu babu tabbaci kan hakan daga gwamnatocin Isra'ila ko Amurka.

    Pakistan, wadda ta kasance babbar kawar Tehran da kuma Washington, ta yi tayin taimakawa wajen sasanta rikicin da ke tsakaninsu.

  9. Iran ta ba jiragen Koriya ta Kudu izinin wucewa ta mashigar Hormuz

    Jakadan Iran a birnin Seoul, Saeed Kozechi, ya bayyana cewa Iran ta ba jiragen ruwan Koriya ta Kudu damar wucewa ta Mashigar Hormuz, idan har sun nemi izini tun da wuri.

    Ya ce Iran ta nemi gwamnatin Seoul da ta riƙa bai wa ƙasar bayanai kan jiragen ruwanta domin a tsara yadda za su bi ta wannan hanya cikin tsari.

    Tun bayan fara rikicin da ya haɗa Iran da Amurka da kuma Isra’ila, da kuma matakin da Iran ta ɗauka na sa ido da sarrafa zirga-zirgar jiragen ruwa a Mashigar Hormuz, wasu jiragen ruwa daga ƙasashen China da Indiya da Japan sun samu damar wucewa ta wannan hanya.

  10. Sojin Amurka sun kai hari kan jirgin ruwan Caribbean

    Rundunar sojin Amurka ta kai hari kan wani jirgin ruwa da take zargin na safarar miyagun ƙwayoyi ne a yankin Caribbean, inda ta kashe mutane huɗu.

    Rundunar a wani saƙo da ta wallafa, ta ce jirgin na kan hanyarsa ta fataucin miyagun ƙwayoyi ne, kuma ta ayyana waɗanda ta kashen a matsayin ƴan ta'adda.

    Gwamnatin Trump dai ta ƙaddamar da hare-hare da dama kan jiragen ruwan da take zargi da safarar miyagun ƙwayoyi, inda ta kashe mutane fiye da 150 daga watan Satumban bara zuwa yanzu.

    Babu dai wata ƙwaƙƙwarar hujja da gwamnatin ke bayarwa kafin kai hare-haren nata.

  11. Iran na ci gaba da kama masu zargin ta’addanci da leƙen asiri a ƙasar

    Ma’aikatar tattara bayanan sirrin Iran ta bayyana cewa ta kama mutum huɗu a jihar Kermanshah kan zargin “shiga ƙungiyar ta’addanci.”

    Mutanen suna shirin kai hari kan cibiyoyin gwamnati “a karkashin jagorancin wani daga Jamus,” in ji ma’aikatar.

    Sanarwar ma’aikatar ta ce an ƙwace bindigogi da bama-bamai da sauran makamai daga hannun waɗannan mutanen.”

    Haka kuma, sanarwar ta bayyana kama wasu “mutane biyar” a jihar Alborz Province da “mutane hudu” a jihar Kerman Province amma ba ta bayyana takamaiman tuhumar da ake musu ba.

    A gefe guda, Mehdi Razzaqinejad, babban lauyan jihar Golestan, ya ce ana tantance “dukiyar mutane 16” kuma za a ƙwace bisa zargin yi wa Amurka da Isra’ila leƙen asiri”

    Iran na ci gaba da kama mutanen da take zargi da alaƙa da ta'addanci da leƙen asiri.

  12. Ƙungiyar tsaron NATO ba ta yi komi ba kan Iran – Trump

    Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake sukar ƙasashen NATO a kafafen sada zumunta, inda ya ce ƙungiyar ba ta yi komai wajen taimakawa Amurka kan yaƙin da take yi da Iran ba kuma ba ta da wani amfani gare shi a wannan lamari.

    A cikin rubutunsa da ya wallafa, Trump ya ce, "Ƙasashen Nato ba suyi komai ba don taimakawa wajen yaƙin da Amurka ke yi da Iran, Amurka ba da buƙatar komai daga Nato, amma kada ku manta da wannan muhimmin lokaci."

    Har yanzu dai yaƙin da Iran ke yi da Amurka da Isra'ila a yankin Gabas ta Tsakiya na ƙara tsananta.

  13. Isra'ila ta ce ta kashe kwamandan rundunar sojin ruwan Iran, Alireza Tangsiri'

    Isra’ila ta bayyana cewa ta kashe kwamandan rundunar sojin ruwan juyin juya halin Iran, Alireza Tangsiri a hare-haren da aka kai a Bandar Abbas.

    Ministan tsaron Isra’ila, Israel Katz, ya ce Tangsiri ne “kai tsaye ke da alhakin kula da mashigar Hormuz tare da kuma rufe ta” kuma an “halaka shi.”

    Ya ƙara da cewa wasu manyan jami’an rundunar sojin ruwa ma sun rasa rayukansu a wannan hari.

    Iran dai har yanzu a su yi tsokaci ba kan wannan lamarin.

  14. WHO ta bayyana damuwa kan halin da ake ciki a Cuba

    Hukumar lafiya ta duniya ta bayyana damuwa kan halin da ake ciki a Cuba, inda ƙarancin mai da katsewar lantaki suka yi mummunan illa ga ɓangaren kiwon lafiya.

    A wani saƙo da ya wallafa a kafafen sada zumunta, shugaban hukumar Tedros Ghebreyesus ya ce dole ne a ɗauki matakin tallafawa asibitocin ƙasar, waɗanda ke fama da rashin wutar lantarki.

    Ya ce: Idan aka cigaba a halin da ƙasar ke ciki yanzu, kuma har ta kai man da take da shi ya ƙare, to lallai akwai hatsarin asarar rayuka.

    Cuba na fama da rashin wutar lantarki saboda katsewar jigilar mai daga Venezuela zuwa ƙasar tun bayan da Amurka ta kama shugaba Nicolas Maduro.

  15. Iran ta kai hare-hare kan cibiyoyin soji da na makaman nukiliyar Isra'ila

    Rundunar juyin juya halin Iran ta bayyana a wata sanarwa cewa ta kai hare-hare kan cibiyoyin soji da kuma masana’antu da ke da alaka da harkokin nukiliyar Isra’ila.

    Rahotanni sun nuna cewa,Iran ta yi amfani amfani da jirage marasa matuƙa da makamai masu linzami wajen kai harin

    Dakarun sojin Isra’ila sun kuma sanar a ‘yan mintuna da suka gabata cewa sun gano sabon harin da Iran ta kai ƙasar da makamai masu linzami.

  16. Ma'aikatan aikin sufuri a Phillippines na yajin aiki kan tashin farashin mai

    Ma'aikatan sufuri a Philippines sun fara yajin aikin kwana biyu a faɗin ƙasar domin nuna adawa da tashin farashin mai saboda rikicin Gabas ta Tsakiya.

    Sun kuma shiga zanga-zanga, inda suke neman gwamnati ta rage farashin man, tare da janye haraji a kan mai da iskar gas.

    Direbobin sun ce tashin farashin man ya matuƙar shafar harkokin rayuwar su. Gwamnatin Philippine dai ta ƙaddamar da tsare-tsaren rage raɗaɗi ga jama'arta da suka haɗa da samar da motocin jigila kyauta, amma masu zanga-zangar sun ce ba su wadatar ba.

    A ranar Talata gwamnati ta ayyana dokar ta ɓaci kan makamashi a ƙasar.

  17. Yadda Lakurawa suka yi wa sojojin Najeriya kwantan ɓauna suka kashe 11

    Ƴan bindiga da aka kyautata zaton Lakurawa ne sun yi wa sojojin Najeriya kwantan ɓauna, inda suka kashe guda 13 tare da jikkata da dama a jihar Kebbi.

    Bayanai sun nuna cewa harin ya faru ne a daren ranar Talatar da ta gabata a garin Giro Masa da ke ƙaramar hukumar Shanga, inda dakarun sojin Najeriya ke ƙoƙarin kai ɗauki bayan samun kira da suka yi daga al'ummar garin.

    Hukumomi na cewa sojojin da aka kashe 11 ne sai kuma jami'in ɗansanda guda ɗaya sai kuma sauran waɗanda suka rasu da samun raunuka da suka haɗa da fararen hular da suka kasance tsakanin sojoji da Lakurawa yayin musayar wuta.

    Kakakin Ć´ansandan jihar ta Kebbi ya shaida wa BBC cewa ba zai iya cewa uffan ba kan farmakin kasancewar abin da ya faru aiki ne na sojoji.

    Gwamnan jihar Kebbi, Nasiru Idris ya kai ziyarar gani da ido zuwa wurin da al'amarin ya faru tare da zuwa asibiti domin duba wadanda suka samu raunuka.

  18. Trump ya tsaya kai da fata cewa yana tattaunawa da Iran

    Shugaban Amurka, Donald Trump ya sake jaddada matsayar sa cewa Iran ta shiga tattaunawar zaman lafiya da su, kuma ta zaƙu a kawo ƙarshen yaƙin da Amurka da Isra'ila suka ƙaddamar a watan jiya.

    Wakilin BBC ya ce: Mr Trump ya ce Iran ta ƙosa a ƙulla yarjejeniyar, amma tana tsoron furta hakan saboda mutanen kasar su za su yi wa mahukunta bore.

    Iran dai ta musanta wannan iƙirari.

    A ranar Laraba ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya ce Amurka ta gabatar da saƙonni kala-kala na neman ƙulla yarjejeniyar zaman lafiya, wani abu da ya ce alamu ne na nasara ga Iran.

  19. Buɗewa

    Masu bibiyarmu barka da war haka a safiyar Alhamis ta 26 ga watan Maris na shekarar 2026. Kamar kullum yau ma mun dawo muku da shafin nan namu mai farin jini da ke kawo muku irin wainar da ake toyawa a Najeriya da sauran sassan duniya kai tsaye.

    Da fatan za ku ci gaba da kasancewa da mu a shafin da ma sauran shafukanmu na sada zumunta.

Trending Now